fidelitybank

Magoya bayan APC dubu guda a Kano sun koma NNPP

Date:

Sama da mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) 1,000 a jihar Kano, sun sauya sheka zuwa jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) a ranar Asabar.

Wadanda suka sauya sheka daga kananan hukumomin Shanono da Bagwai sun samu tarba ne daga mataimakin gwamna Aminu Abdussalam Gwarzo a madadin gwamna Abba Kabir Yusuf a fadar gwamnatin jihar Kano.

Wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin gwamnan, Ibrahim Garba Shuaibu ya fitar ya bayyana jin dadin Gwarzo na maraba da masu sauya shekar.

Ya kuma jaddada cewa jam’iyyar NNPP ta ba da fifiko kan hadin kai, kuma za a yi wa dukkan mambobin kungiyar adalci.

A cewar Garba, Gwarzo ya jaddada kudirin gwamnatin na aiwatar da shirye-shiryen da za su amfani daukacin al’ummar Jihar Kano, ya kuma bukaci ci gaba da bayar da goyon baya daga mazauna jihar domin ci gaban jihar.

Da yake jawabi tun da farko, shugaban masu sauya shekar, Alhaji Haruna Babangida Abbas (Kosashe), ya bayar da misali da halayen shugabanci da salon mulkin Gwamna Abba a matsayin dalilan da suka sa suka dauki wannan mataki.

Ya nuna nadamarsu ga jam’iyyar APC a baya tare da yin alkawarin yin aiki da NNPP domin ci gaban Kano.

Shima da yake jawabi, Shugaban NNPP na Kano, Alhaji Hashimu Dungurawa ya yi maraba da sabbin ‘ya’yan jam’iyyar tare da ba da tabbacin shiga ayyukan jam’iyyar.

Ya kuma ja hankalin ‘ya’yan sauran jam’iyyu ciki har da APC da su shiga jam’iyyar NNPP domin ci gaban jihar.

Dungurawa ya kuma bukaci goyon bayan manufofin gwamnati.

Taron ya samu halartar manyan mutane, kamar kwamishinan kasafi da tsare-tsare na jihar Kano, Alhaji Musa Suleiman Shanono, da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar NNPP da dama wadanda suka yi murnar shigowar sabbin mambobin kungiyar.

jalingo news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp