fidelitybank

Magoya bayan APC dubu guda a Kano sun koma NNPP

Date:

Sama da mambobin jam’iyyar All Progressives Congress (APC) 1,000 a jihar Kano, sun sauya sheka zuwa jam’iyyar New Nigeria People’s Party (NNPP) a ranar Asabar.

Wadanda suka sauya sheka daga kananan hukumomin Shanono da Bagwai sun samu tarba ne daga mataimakin gwamna Aminu Abdussalam Gwarzo a madadin gwamna Abba Kabir Yusuf a fadar gwamnatin jihar Kano.

Wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin gwamnan, Ibrahim Garba Shuaibu ya fitar ya bayyana jin dadin Gwarzo na maraba da masu sauya shekar.

Ya kuma jaddada cewa jam’iyyar NNPP ta ba da fifiko kan hadin kai, kuma za a yi wa dukkan mambobin kungiyar adalci.

A cewar Garba, Gwarzo ya jaddada kudirin gwamnatin na aiwatar da shirye-shiryen da za su amfani daukacin al’ummar Jihar Kano, ya kuma bukaci ci gaba da bayar da goyon baya daga mazauna jihar domin ci gaban jihar.

Da yake jawabi tun da farko, shugaban masu sauya shekar, Alhaji Haruna Babangida Abbas (Kosashe), ya bayar da misali da halayen shugabanci da salon mulkin Gwamna Abba a matsayin dalilan da suka sa suka dauki wannan mataki.

Ya nuna nadamarsu ga jam’iyyar APC a baya tare da yin alkawarin yin aiki da NNPP domin ci gaban Kano.

Shima da yake jawabi, Shugaban NNPP na Kano, Alhaji Hashimu Dungurawa ya yi maraba da sabbin ‘ya’yan jam’iyyar tare da ba da tabbacin shiga ayyukan jam’iyyar.

Ya kuma ja hankalin ‘ya’yan sauran jam’iyyu ciki har da APC da su shiga jam’iyyar NNPP domin ci gaban jihar.

Dungurawa ya kuma bukaci goyon bayan manufofin gwamnati.

Taron ya samu halartar manyan mutane, kamar kwamishinan kasafi da tsare-tsare na jihar Kano, Alhaji Musa Suleiman Shanono, da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar NNPP da dama wadanda suka yi murnar shigowar sabbin mambobin kungiyar.

legit news.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp