fidelitybank

Magidanci ya ƙwaƙwulewa matarsa kayan ciki a Jos

Date:

Ana zargin wani mutum mai shekara 32 da kashe matarsa mai suna Mercy Samuel a Jos a jihar Filato.

Hukumomin jihar Filato sun tabbatar da faruwar lamarin, inda Kwamishiniyar kula da harakokin mata ta jihar Rebecca Sambo ta shaida wa BBC Pidgin cewa, lamarin ya faru ne a daren 17 ga watan Afrilu.

Ta ce mijin ya yaga cikin matarsa misalin ƙarfe biyu na dare ya cire ƴan hanjinta.

Matar ƴar shekara 25 ta mutu bayan an garzaya da ita zuwa asibitin koyarwa na Jami’ar Bingham a Jos domin yi mata tiyata.

Rundunar ƴan sandan Filato ta ce tana kan gudanar da bincike game da al’amarin.

Mercy da mijinta sun yi aure tsawon shekara tara kuma sun haifi ƴaƴa biyu.

Dan uwanta ya ce cikin dare makwabta suka ji tana ihu, ko da aka fito sai ga ƴan hanjin cikinta a hannunta.

Yanzu haka ƴan sanda na farautar mijin wanda ya gudu.

news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...
X whatsapp