Rundunar ‘yan sandan jihar Bauchi ta kaddamar da bincike kan wata mata ‘yar shekara 24 da ta mutu, da ake zargin mijinta dan shekara 50 ya yi mata dukan tsiya har ta mutu a wani rikici da ya barke a cikin gida kan shirin abinci na watan Ramadan.
A cewar wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, CSP Ahmed Wakili ya fitar, ta ce lamarin ya faru ne a ranar 1 ga Maris, 2025, da misalin karfe 11:30 na dare a unguwar Fadamam Mada, kusa da Kwalejin ’yan mata ta gwamnati, Bauchi.
Rahotanni sun bayyana cewa wanda ake zargin Alhaji Nuru Isah, wani dan kasuwa ne a babbar kasuwar Bauchi, ya kai wa matarsa ta biyu Wasila Abdullahi hari, bayan da suka samu sabani kan kayan abinci da kuma ‘ya’yan itatuwa da aka tanada domin karya azumin watan Ramadan.
Rikicin ya yi kamari, inda aka ce Isah ya bugi Wasila da sara, wanda hakan ya sa ta ruguje, ta kuma rasa hayyacinta a cikin gidansu.
An garzaya da ita asibitin koyarwa na ATBU, inda jami’an lafiya suka tabbatar da rasuwar ta.
“’Yan sanda sun kama wanda ake zargin tare da kwato sandar da aka yi amfani da ita wajen kai harin a matsayin shaida.
“An ajiye gawar wanda aka kashe a dakin ajiyar gawarwaki har zuwa lokacin da za a gudanar da bincike.
“Kwamishanan ‘yan sandan jihar Bauchi, CP Auwal Musa Muhammad, ya tabbatar wa jama’a cewa za a yi adalci.
Sanarwar ta kara da cewa “Ya kuma yi amfani da damar wajen jaddada illolin tashin hankalin cikin gida, inda ya yi kira ga al’umma da su kiyaye mutuntawa, tausayawa, da fahimtar juna a rayuwar iyali.”
Rundunar ‘yan sandan ta bukaci mazauna yankin da su kai rahoto game da cin zarafi a cikin gida, tare da jaddada cewa tashin hankali a cikin gida laifi ne da ke da babban sakamako.