fidelitybank

Magidanci ya mutu garin ceto dansa da ya fada cikin rijiya

Date:

Hukumar kashe gobara ta jihar Kwara, a ranar Alhamis din da ta gabata, ta gano gawar wani mutum mai shekaru 49, tare da ceto wani yaro dan shekara 17 a rijiyar gidansa a garin Offa.

Mutumin mai suna Fasasi Afeez, da dansa Kaleed Afeez na Gaa Jangbo, Igbonna Road Offa, a karamar hukumar Offa ta jihar Kwara, sun fada cikin rijiya.

Sai dai yayin da aka tsinci gawar mutumin, an ceto dan da ransa.

A cewar kakakin hukumar kashe gobara ta jihar, Hassan Adekunle, lamarin ya faru ne da misalin karfe 04:11 na rana, kuma an gayyaci birgediya ta wayar tarho da wani Alhaji Taiye Gbadamosi da ke zaune a unguwar.

A cewar wani rahoto, “Yaron da aka ceto ya je diban ruwa daga rijiyar cikin gida, kuma ana cikin diban ruwa ne, sai ga wata kafarsa ta zame daga kasa, a karshe ya fada cikin rijiyar.

“Duk da haka, kafin isowar jami’an kashe gobara, mahaifinsa a lokacin da yake kokarin ceto wanda abin ya shafa, kwatsam kafafunsa sun zame daga kasa kuma daga karshe ya fada cikin rijiyar.”

Daraktan Hukumar Kashe Gobara ta Jihar Kwara, Prince Falade John Olumuyiwa, ya bayyana alhininsa game da faruwar lamarin, ya kuma bukaci jama’a da su kara kula da harkokinsu na yau da kullum, su guji tura yara masu karancin shekaru zuwa debo ruwa a rijiyoyin gida.

latest news in nigeria today 2022 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp