fidelitybank

Magidanci ya mutu a ramin Shadda wajen dako wayarsa da ta fada a Kano

Date:

Wani mutum mai suna Mu’azu Garba a jihar Kano ya mutu a lokacin da yake kokarin dako wayarsa da ta fada ramin shadda na bayi.

Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis a garin Jigirya da ke karamar hukumar Nassarawa a jihar Kano.

Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Abdullahi ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar.

Da yake bayyana lamarin, Abdullahi ya ce, hukumar ta samu wani kira a ranar Alhamis da misalin karfe 1:35 na rana daga wani Abbas Abubakar, inda ya ce, wani mutum ya makale a cikin ramin shadda.

Ya ce, mutumin mai shekaru 40 da haifuwa yana kokarin fito da wayarsa da ta fada cikin ramin, amma ya kasa fitowa daga cikin ramin.

“Nan da nan muka aika da tawagar mu zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 1:45 na rana,” in ji Abdullahi.

Sai dai ya ce an fito dashi a macce, kuma an mika gawarsa ga hakimin unguwar Jigirya, Nuhu Adamu.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...

Sojoji sun mayar da martani kan ‘Yan ta’addan Neja

Dakarun Sojin Saman kasar nan, sun ce sun ƙaddamar...

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...
X whatsapp