Wani mutum mai suna Mu’azu Garba a jihar Kano ya mutu a lokacin da yake kokarin dako wayarsa da ta fada ramin shadda na bayi.
Lamarin ya faru ne a ranar Alhamis a garin Jigirya da ke karamar hukumar Nassarawa a jihar Kano.
Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Abdullahi ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar.
Da yake bayyana lamarin, Abdullahi ya ce, hukumar ta samu wani kira a ranar Alhamis da misalin karfe 1:35 na rana daga wani Abbas Abubakar, inda ya ce, wani mutum ya makale a cikin ramin shadda.
Ya ce, mutumin mai shekaru 40 da haifuwa yana kokarin fito da wayarsa da ta fada cikin ramin, amma ya kasa fitowa daga cikin ramin.
“Nan da nan muka aika da tawagar mu zuwa wurin da abin ya faru da misalin karfe 1:45 na rana,” in ji Abdullahi.
Sai dai ya ce an fito dashi a macce, kuma an mika gawarsa ga hakimin unguwar Jigirya, Nuhu Adamu.