Wani magidanci ya shiga hannun mahukunta, bayan ya daba wa mahaifiyarsa wuka, bisa kuskure a Zawiyya Tudunwada da ke garin Kontagora, jihar Neja.
Rahotanni na cewa, magidancin na fada ne da matarsa lokacin da mahaifiyar tasa ta iso domin shiga tsakani.
Hakazalika an kwashi matar wacce ta ji raunuka daban-daban sakamakon dukan da mijin ya yi mata zuwa asibiti. A cewar Legit.
Rahoton ya kuma kawo cewa an kama magidancin bayan labarin mutuwar mahaifiyar tasa ya fita.