fidelitybank

Magidanci ya kai karar Matarsa bayan ta canja sunayen ‘ya’yan su zuwa na Masoyinta

Date:

Ayodeji Obayan, mai matsakaicin shekaru, a ranar Juma’a, ya garzaya kotun al’ada ta Grade ‘A’ da ke Oke-Eda, Akure, Jihar Ondo, inda ya nemi mahaifar ‘ya’yansa hudu da ta dawo da sunayen su kamar yadda yake a baya maimakon sabon masoyinta.

Matakin na zuwa ne bayan matar sa Lillian Obayan ta bayyana cewa ta sauya sunayen ‘ya’yansu domin ya dace da sunan sabuwar masoyinta.

Obayan, wanda ya nuna matukar bacin ransa kan lamarin, ya sha alwashin bin doka da oda domin tabbatar da hakkinsa a matsayin uban ‘ya’yansa.

A cewarsa, ya yanke shawarar garzaya kotu domin neman taimakonta biyo bayan matakin da matarsa ta dauka na sauya sunayen ‘ya’yansu ba tare da izininsa ba.

A lokacin da ya ke ba da shaida a gaban kotu, Obayan ya bayyana cewa auren nasu da ya shafe shekaru 23 yana fama da rikici da cin zarafi akai-akai.

Ya bayyana cewa a cikin 2019, Lillian ta kwashe kayanta kuma ta bar gidansu don shiga tare da wani mutum.

A cewarsa, abin da ya kara ta’azzara shi ne, matar da ya rabu ta canza ba kawai sunanta ba, har ma da sunayen ‘ya’yansu domin ya dace da sunan sabon masoyinta.

A nata bangaren, Lilian ta bayyana Obayan a matsayin wanda ba shi da alhaki, “Obayan ba mijin kirki ba ne a gare ni, kuma uba nagari ga ’ya’yansa, domin ba ya biyan kudin makaranta, kuma ba ya kula da yadda suke rayuwa.

“Bai biya sadakina ba. Don haka, daga karshe na sami namiji da zan aura. Kuma sabuwar soyayyata tana son ’ya’yana su riƙa ɗaukan sunansa maimakon na ubansu mara nauyi.

“Yaranmu sun isa zabar wa kansu tunda ba yara ba ne. ’Yan mata biyu na farko, Mayomi da Damilola, ‘yan shekara 22 da 20, yayin da yaran maza, Ariyo da Aduragbemi, ‘yan shekara 18 da 16 ne.”

A halin da ake ciki, a hukuncin da ya yanke, shugaban kotun, Majistare Olusegun Rotiba, ya roki bangarorin da su bar zaman lafiya ya wanzu a tsakaninsu.

Daga baya ya dage sauraron karar har zuwa ranar 28 ga Satumba, 2023, don ci gaba da karbar adireshi na baka da kuma yiwuwar yanke hukunci.

the nation newspaper nigeria today latest

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp