Ayodeji Obayan, mai matsakaicin shekaru, a ranar Juma’a, ya garzaya kotun al’ada ta Grade ‘A’ da ke Oke-Eda, Akure, Jihar Ondo, inda ya nemi mahaifar ‘ya’yansa hudu da ta dawo da sunayen su kamar yadda yake a baya maimakon sabon masoyinta.
Matakin na zuwa ne bayan matar sa Lillian Obayan ta bayyana cewa ta sauya sunayen ‘ya’yansu domin ya dace da sunan sabuwar masoyinta.
Obayan, wanda ya nuna matukar bacin ransa kan lamarin, ya sha alwashin bin doka da oda domin tabbatar da hakkinsa a matsayin uban ‘ya’yansa.
A cewarsa, ya yanke shawarar garzaya kotu domin neman taimakonta biyo bayan matakin da matarsa ta dauka na sauya sunayen ‘ya’yansu ba tare da izininsa ba.
A lokacin da ya ke ba da shaida a gaban kotu, Obayan ya bayyana cewa auren nasu da ya shafe shekaru 23 yana fama da rikici da cin zarafi akai-akai.
Ya bayyana cewa a cikin 2019, Lillian ta kwashe kayanta kuma ta bar gidansu don shiga tare da wani mutum.
A cewarsa, abin da ya kara ta’azzara shi ne, matar da ya rabu ta canza ba kawai sunanta ba, har ma da sunayen ‘ya’yansu domin ya dace da sunan sabon masoyinta.
A nata bangaren, Lilian ta bayyana Obayan a matsayin wanda ba shi da alhaki, “Obayan ba mijin kirki ba ne a gare ni, kuma uba nagari ga ’ya’yansa, domin ba ya biyan kudin makaranta, kuma ba ya kula da yadda suke rayuwa.
“Bai biya sadakina ba. Don haka, daga karshe na sami namiji da zan aura. Kuma sabuwar soyayyata tana son ’ya’yana su riƙa ɗaukan sunansa maimakon na ubansu mara nauyi.
“Yaranmu sun isa zabar wa kansu tunda ba yara ba ne. ’Yan mata biyu na farko, Mayomi da Damilola, ‘yan shekara 22 da 20, yayin da yaran maza, Ariyo da Aduragbemi, ‘yan shekara 18 da 16 ne.”
A halin da ake ciki, a hukuncin da ya yanke, shugaban kotun, Majistare Olusegun Rotiba, ya roki bangarorin da su bar zaman lafiya ya wanzu a tsakaninsu.
Daga baya ya dage sauraron karar har zuwa ranar 28 ga Satumba, 2023, don ci gaba da karbar adireshi na baka da kuma yiwuwar yanke hukunci.