fidelitybank

Magidanci ya ƙwaƙwulewa matarsa kayan ciki a Jos

Date:

Ana zargin wani mutum mai shekara 32 da kashe matarsa mai suna Mercy Samuel a Jos a jihar Filato.

Hukumomin jihar Filato sun tabbatar da faruwar lamarin, inda Kwamishiniyar kula da harakokin mata ta jihar Rebecca Sambo ta shaida wa BBC Pidgin cewa, lamarin ya faru ne a daren 17 ga watan Afrilu.

Ta ce mijin ya yaga cikin matarsa misalin ƙarfe biyu na dare ya cire ƴan hanjinta.

Matar ƴar shekara 25 ta mutu bayan an garzaya da ita zuwa asibitin koyarwa na Jami’ar Bingham a Jos domin yi mata tiyata.

Rundunar ƴan sandan Filato ta ce tana kan gudanar da bincike game da al’amarin.

Mercy da mijinta sun yi aure tsawon shekara tara kuma sun haifi ƴaƴa biyu.

Dan uwanta ya ce cikin dare makwabta suka ji tana ihu, ko da aka fito sai ga ƴan hanjin cikinta a hannunta.

Yanzu haka ƴan sanda na farautar mijin wanda ya gudu.

nigeria newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta yanke wa Matashin da ya kashe Budurwarsa hukuncin kisa

Kotun babban birnin jihar Nasarawa ta yanke wa wannan...

PDP ta yi watsi da matakin shugaban jam’iyyar da ya dauka

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP, ya yi watsi da...

Tinubu zai sanya hannu kan sabbin dokokin haraji

Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai sanya hannu kan...

‘Yan Bindiga sun kashe Sojoji a Neja

Rundunar Sojin Kasa, ta tabbatar da mutuwar wasu daga...

Kungiyoyi 110 suna bukatar mu yi musu rijista – INEC

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta tabbatar da samun buƙatu...

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...
X whatsapp