fidelitybank

Magidanci da Matarsa sun rasu yayin jin ɗumi a Kano

Date:

Rundunar ‘yan sanda a Kano, ta tabbatar da mutuwar mata da miji a gidansu.

Ma’auratan sun gamu da akalin su ne a kauyen Kwa da ke karkashin karamar hukumar Dawakin Tofa a jihar.

Ana kyautata zaton ma’auratan sun mutu ne sakamakon shakewar hayakin gawayi.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna-Kyawa ya bayyana wadanda suka mutun a matsayin Sulaiman Idris mai shekaru 28 da Maimuna Haliru mai shekaru 20.

PRO ya ce bayan babu wanda ya ji ta bakinsu, kakar Idris ta tilastawa bude kofa, ta tarar da su biyun ba su da motsi.

Tawagar jami’an ‘yan sanda karkashin jagorancin CSP Ahmed Hamza DPO DPO na Dawakin Tofa sun zarce zuwa wurin.

An garzaya da gawarwakin zuwa asibitin kwararru na Murtala Muhammed inda wani likita ya tabbatar da mutuwar su.

Haruna-Kiyawa ya lura cewa, ma’auratan sun kunna wutar ts gawayi don dumama dakin saboda yanayin sanyi.

Kakakin ya kara da cewa, “Sun kulle kuma hayakin da ke fitowa daga garwashin gawayi ya shafe su,” in ji kakakin.

bbc news 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnan Kano ya kori mataimansa na musamman kan belin Danwawu

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya amince da...

Tsohon Minista a mulkin Buhari ya mutu

Allah ya yi wa tsohon ministan noma da raya...

Kashi 70 na yankin Bukuyum ta Kudu na ƙarƙashin ƴan Bindiga – Ɗan majalisa

Rahotanni daga yakin ƙaramar hukummar Bukuyum na jihar Zamfara...

Goodluck ya fi dacewa ya zama dan takara a 2027 – Lamido

Tsohon Gwamnan jihar Jigawa, Sule Lamido ya ce Tsohon...

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...
X whatsapp