Tukur Buratai, tsohon babban hafsan sojin kasa (COAS), ya ce, akwai bukatar a kara kafa sansanonin soji a fadin Najeriya domin yaki da matsalar tsaro.
Mista Buratai, wanda kuma jakadan Najeriya a jamhuriyar Benin ne ya bayyana haka a lokacin da yake kaddamar da wata kofar makaranta da wata hanya da aka sanya masa suna a makarantar Command Science Secondary School da ke Saki a jihar Oyo.
Ya jaddada cewa, Najeriya na bukatar karin sansanonin soji, ba wai a aikin soja kadai ba, har ma da sauran ayyuka, musamman a lokacin da kasar ke fama da matsalar rashin tsaro.
“A wannan zamanin na ta’addanci, tada kayar baya, yakin basasa, akwai bukatar a yada jami’an tsaro don kula da wuraren da ba su da yawa, wadanda ke bukatar daukar matakan gaggawa.
“Na hango kafa wasu sansanonin soji a yankin.