Wanda ya yi garkuwa da Hanifa ‘yar shekara biyar tare da kashe ta ya kuma binne ta a makarantar sa, ya ce, maganin Bera na Naira dari ya baiwa marigayira ta sha ta mutu.
Abdulmalik Muhammad Tanko, ya bayyana hakan ne yayin holin sa da rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta yi a shalkwatar ta da ke Bompai.
Ya ce“Maganin Bera na Naira 100 kawai na baiwa Hanifa ta sha, sannan nan ta mutu, ni kuma na saka ta a cikin buhu na binne ta a cikin makaranta”.
Da aka tambaye shi ko ya na da iyali sai ya ce“Tabbas, ina da ‘ya’ya mata uku nima”. In ji Abdulmalik.