fidelitybank

Mafarauta sun ceto Jariri da ransa bayan an binne shi a Benue

Date:

Wasu mafarauta a yankin Benuwe sun ceto wani jariri da aka ce binne shi da ransa a karamar hukumar Buruku ta jihar.

A cewar wani mazaunin yankin, wanda kawai ya bayyana kansa da Terna, lamarin ya faru ne a unguwar Ashav Kusuv.

Ya bayyana cewa mafarauta ne suka gano jaririyar suka kawo ta da rai daga dajin da aka binne ta da ranta.

“Wasu mafarauta a ranar Asabar sun gano wata jaririya, suka ce sun same ta a binne da ranta a wani daji.

“A halin yanzu ana kula da jaririn a unguwar Ashav Kusuv,” in ji shi.

Shugaban karamar hukumar Iorkyaan Aberg, da yake zantawa da manema labarai a ranar Lahadi, ya tabbatar da labarin, inda ya bayyana cewa wasu mafarauta ne suka gano jaririn a wani daji.

Agba ya bayyana cewa, “Hakika wasu mafarauta sun sami jariri a cikin dajin amma muna kan bincike don sanin wanda ya je ya jefar da jariri a cikin dajin da kuma dalilin yin hakan.”

Har zuwa lokacin da ake wannan rahoto, kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ‘yan sandan Binuwai, Catherine Anene bai yi nasara ba, yayin da wayarta ta ci karo.

www.leadership ng.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp