Manchester City za ta gwabza da Real Madrid a neman tsallake wa zuwa gurbin ƴan 16 na Gasar Zakarun Turai.
Celtic kuma za ta fafata da Bayern Munich .
City da ta lashe Champions League a 2023, za ta karɓi bakuncin Real a filin wasanta na Etihad tsakanin 11 ko 12 na watan Febrairu, kafin balaguro zuwa Sifaniya makon da zai biyo baya.
Haka kuma Bayern Munich za ta ziyarci Celtic a zagaye na farko kafin ta karɓi bakuncinsu a Allianz Arena a wasan zagaye na biyu.
Ga yadda sauran jadawalin ƙungiyoyin ya kasance:
- Brest v Paris St-Germain
- Club Brugge v Atalanta
- Manchester City v Real Madrid
- Juventus v PSV
- AS Monaco v Benfica
- Sporting v Borussia Dortmund
- Celtic v Bayern Munich
- Feyenoord v AC Milan