Rahotanni daga kasar Sipaniya sun bayyana cewa, kungiyar kwallon kafa ta Real Madrid ta gano wasu ‘yan wasa uku da zasu maye gurbin tsohon dan wasan gaba, Karim Benzema a tsakiyar kasuwar saye da sayar da ‘yan wasa na watan Janairu.
Benzema har yanzu yana kan kololuwar ikonsa duk da yana da shekaru 35 a duniya.
Dan wasan na Faransa ya lashe kyautar gwarzon dan kwallon kafa ta Ballon d’Or a kakar wasan da ta wuce saboda bajintar da ya yi a Real Madrid.
Benzema ya zura kwallaye 44 sannan ya taimaka aka zura kwallaye 15 a wasanni 46 da ya buga a Los Blancos a kakar wasan da ta wuce don taimakawa Los Blancos lashe gasar La Liga ta Spain da kuma gasar zakarun Turai.
Yayin da Benzema ke ci gaba da kasancewa daya daga cikin ‘yan wasan gaba da ake fargabar a nahiyar Turai, rahotanni sun ce Real Madrid ta sanya hannu kan ‘yan wasa uku da za su maye gurbinsa a nan gaba.
A cewar Fichajes, ‘yan wasan ukun sune matashin dan kasar Brazil Endrick, na Manchester City Erling Haaland da kuma Rafael Leao na AC Milan.
Tuni dai Real Madrid ta kammala siyan Endrick wanda zai koma kungiyar daga Palmeiras a shekarar 2024.