fidelitybank

Mace ta kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su a Filato

Date:

Wata mata mai suna Lucy Tapnang, ‘yar shekara 29 da haihuwa ta kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su tare a Filato.

Matar wadda wasu ‘yan bindiga suka sace tare da wasu mutum uku, ta yi ta maza inda ta kwace bindiga samfurin AK47 daga hannun daya daga cikin wadanda suka sace su, to amma duk da haka sai da suka ji mata rauni da wuka.

Lucy wadda mazauniyar Abuja babban birnin tarayyar Najeriya ce, na kan hanyarta ne ta zuwa karamar hukumar Mangu tare da wasu fasinjoji bakwai a cikin motar, a nan ne ‘yan bindiga suka tare su.

Lucy ta shaida wa shalkwatar ‘yan sanda da ke Jos cewa, lamarin abin tsoro da tashin hankali ne.

Ta ce,” A dai dai lokacin da muka kusa isa makarantar kimiyya ta Kuru, sai kawai muka ga wasu mutane sun tsayar da motar da muke ciki.Nan na ga wani mutum da bindiga a cikinsu yana kuma umartar duk mutanen motar mu sauka muka kuma mika wayoyin salularmu da kudi.A lokacin sai kawai na ce da fasinjojin motar ku fa maza ne yakamata mu yi ta maza don mu ceci kanmu, to amma sai suka ce mini ai mutanen na da bindiga kada su illatar da su.”

To daga nan ne ita ta yi mazan ta wufce bindigar da ke hannun daya daga cikin masu satar mutanen in ji mai magana da yawun ‘yan sanda jihar Alfred Alabo, wanda ya tabbatar da afkuwar lamarin.

Ya ce, sauran fasinjojin ma sun taimaka mata bayan da suka ga ta kwace bindigar mutum guda.

Jami’in dan sandan ya ce ko da suka samu labarin harin sai suka aika jami’ansu ba tare da bata lokaci ba aka ceto mutanen.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta É—aure Matashin da ya shiga É—akin kwanan ÆŠalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaÆ™i don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin Æ™era nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe Æ´an Æ™asarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faÉ—a kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta Æ™addamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo Æ™arshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar Æ´ansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin Æ´an Æ™asarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp