Wata mata mai suna Lucy Tapnang, ‘yar shekara 29 da haihuwa ta kubutar da mutanen da aka yi garkuwa da su tare a Filato.
Matar wadda wasu ‘yan bindiga suka sace tare da wasu mutum uku, ta yi ta maza inda ta kwace bindiga samfurin AK47 daga hannun daya daga cikin wadanda suka sace su, to amma duk da haka sai da suka ji mata rauni da wuka.
Lucy wadda mazauniyar Abuja babban birnin tarayyar Najeriya ce, na kan hanyarta ne ta zuwa karamar hukumar Mangu tare da wasu fasinjoji bakwai a cikin motar, a nan ne ‘yan bindiga suka tare su.
Lucy ta shaida wa shalkwatar ‘yan sanda da ke Jos cewa, lamarin abin tsoro da tashin hankali ne.
Ta ce,” A dai dai lokacin da muka kusa isa makarantar kimiyya ta Kuru, sai kawai muka ga wasu mutane sun tsayar da motar da muke ciki.Nan na ga wani mutum da bindiga a cikinsu yana kuma umartar duk mutanen motar mu sauka muka kuma mika wayoyin salularmu da kudi.A lokacin sai kawai na ce da fasinjojin motar ku fa maza ne yakamata mu yi ta maza don mu ceci kanmu, to amma sai suka ce mini ai mutanen na da bindiga kada su illatar da su.”
To daga nan ne ita ta yi mazan ta wufce bindigar da ke hannun daya daga cikin masu satar mutanen in ji mai magana da yawun ‘yan sanda jihar Alfred Alabo, wanda ya tabbatar da afkuwar lamarin.
Ya ce, sauran fasinjojin ma sun taimaka mata bayan da suka ga ta kwace bindigar mutum guda.
Jami’in dan sandan ya ce ko da suka samu labarin harin sai suka aika jami’ansu ba tare da bata lokaci ba aka ceto mutanen.