fidelitybank

Mace ta farko ta zama shugabar majalisar yara ta Kano

Date:

Wata daliba ‘yar shekara 16 daga makarantar Kano Capital Girls da ke jihar Kano, Hauwa’u Ibrahim Muhammad a ranar Larabar da ta gabata ta zama mace ta farko da ta zama shugabar majalisar yara ta Kano karo na hudu.

Hauwa’u, dalibar SS 2 daga karamar hukumar Nassarawa ta samu nasarar lashe zabe, bayan ta samu kuri’u 38 yayin da babban abokin hamayyarta, Sadiq Muhammad Ghali daga GSS, Gwale ya samu kuri’u 30.

Musa ya ce adadin yara 81 ne suka yi rajista kuma suka kada kuri’a a zaben.

“Akwai mukamai 10 da aka zaba. Muna da adadin mutane 81 da suka yi rajista da masu kada kuri’a a lokacin zaben.

Sauran manyan hafsoshin da aka zaba sun hada da, Mustapha Sunusi Sani a matsayin shugaban majalisar wakilai, Habiba Aliyu (Mataimakin shugaban majalisar wakilai), Muhammad Yasin (shugaban masu shari’a), Hamza Nasiru Ado (mataimakin shugaban masu shari’a), Ummulkhair Mahmud (Malaci), Ibrahim Abdullahi (Mataimakin Clerk), Hauwa’u Nasir Nuhu da Hassan Abubakar a matsayin Mace Bearer da mataimakiyar Mace Bearer bi da bi.

Yaran da suka fito daga makarantun gwamnati na kananan hukumomi 44 na jihar kuma masu shekaru tsakanin 12 zuwa 16 ne suka hallara, domin zabar manyan jami’ansu da za su jagoranci harkokin majalisar yara na tsawon shekaru uku masu zuwa.

Gwamnatin jihar Kano ce, ta shirya zaben tare da goyon bayan Expanding Social Protection for Inclusive Development, ESPID and Rule of Law and Anti-Corruption, RoLac. A cewar Vanguard.

A jawabinta na karba, sabuwar kakakin majalisar, Hauwa’u Ibrahim Muhammad ta yi alkawarin ci gaba da gudanar da ayyukanta na shugaban majalisar.

Ta kuma yi alkawarin cewa, shugabancinta zai inganta kan halin da kananan yara ke ciki a jihar.

mmm.nnn.

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp