Bayan kama shugaban kungiyar kwadago ta NLC, Joe Ajaero, kungiyar ta sanya dukkan ma’aikatan Najeriya da sauran kungiyoyin kwadago su zama cikin shirin ko-ta-kwana.
Jamiāan tsaro na farin kaya, DSS, sun kama Ajaero a safiyar ranar Litinin.
An dauke shi ne a filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe International Airport, Abuja, a lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa kasar Ingila, domin gudanar da aiki a hukumance, sai jamiāan DSS suka dauke shi.
A wata sanarwa da ta fitar a hukumance X, NLC ta bukaci a gaggauta sakin shugabanta na kasa.
“Muna bukatar a gaggauta sakin shugaban majalisar, Comrade Joe Ajaero ba tare da wani sharadi ba,” kamar yadda ta rubuta.
Kungiyar ta kuma bukaci dukkanin kungiyoyin da ke da alaka da su, da majalisun jihohi, da kungiyoyin farar hula da kuma duk āyan Najeriya masu kishin kasa su kasance cikin shiri.
A kwanakin baya rundunar āyan sandan Najeriya ta gayyaci shugaban kungiyar ta NLC domin amsa tambayoyi kan zargin alaka da bayar da kudaden taāaddanci da dai sauran laifuka.
Kungiyar, bayan gayyatar, ta sha alwashin rufe tattalin arzikin kasar idan aka kama Ajaero.