fidelitybank

Ma’aikatu da kungiyoyi ku zama cikin shirin ko-ta-kwana – Kungiyar Kwadago

Date:

Bayan kama shugaban kungiyar kwadago ta NLC, Joe Ajaero, kungiyar ta sanya dukkan ma’aikatan Najeriya da sauran kungiyoyin kwadago su zama cikin shirin ko-ta-kwana.

Jami’an tsaro na farin kaya, DSS, sun kama Ajaero a safiyar ranar Litinin.

An dauke shi ne a filin jirgin sama na Nnamdi Azikwe International Airport, Abuja, a lokacin da yake kan hanyarsa ta zuwa kasar Ingila, domin gudanar da aiki a hukumance, sai jami’an DSS suka dauke shi.

A wata sanarwa da ta fitar a hukumance X, NLC ta bukaci a gaggauta sakin shugabanta na kasa.

“Muna bukatar a gaggauta sakin shugaban majalisar, Comrade Joe Ajaero ba tare da wani sharadi ba,” kamar yadda ta rubuta.

Kungiyar ta kuma bukaci dukkanin kungiyoyin da ke da alaka da su, da majalisun jihohi, da kungiyoyin farar hula da kuma duk ā€˜yan Najeriya masu kishin kasa su kasance cikin shiri.

A kwanakin baya rundunar ā€˜yan sandan Najeriya ta gayyaci shugaban kungiyar ta NLC domin amsa tambayoyi kan zargin alaka da bayar da kudaden ta’addanci da dai sauran laifuka.

Kungiyar, bayan gayyatar, ta sha alwashin rufe tattalin arzikin kasar idan aka kama Ajaero.

sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Zan cigaba da sa yawan jini ga maʙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...

A shirye nake na mutu don nasarar APC a 2027 – Orji Kalu

Sanatan Abia ta Arewa, Orji Uzor Kalu, ya bayyana...

Bayan hutun Sallah Tinubu zai koma Abuja

Shugaban ʙasa, Bola Tinubu na kan hanyarsa ta komawa...

Mutane 570 aka kashe a Najeriya cikin watan Afrilu – Rahoto

Hukumar kare haʙʙin ɗan'adam a Najeriya ta ce, adadin...

PDP ba za ta mutu ba duk da rikicin cikin gida – Wike

Ministan babban birnin tarayya Abuja, Nyesom Wike ya ce...

Sojoji sun kashe riʙaʙen ɗan bindiga Guddel a Kaduna

Sojoji sun yi nasarar kawar da fitaccen shugaban ā€˜yan...

Fadar shugaban ʙasa ta yi kakkausar gargaɗi a kan Ndume

Fadar shugaban kasa ta yi kakkausar gargadi ga dan...

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ʙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ʙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ʓan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baʙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...
X whatsapp