fidelitybank

Ma’aikatana ku baiwa Tinubu goyon baya – Osibanjo

Date:

Mataimakin shugaban kasa, Yemi Osinbajo ya umurci dukkan ma’aikatan ofishin sa wadanda ke cikin jam’iyyar All Progressives Congress, APC, Presidential Campaign Council, PCC, da su baiwa dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar, Bola Tinubu iyakar kokarinsu.

Osinbajo ya bayar da umarnin ne a wata ganawa da ma’aikatan sa wadanda ke cikin kwamitin na PCC.

Da yake bayyana hakan, mai taimaka wa shugaban kasa Muhammadu Buhari, Ajuri Ngelale, ya ce Osinbajo ya jaddada muhimmancin aikin.

Ngelale, wanda yana daya daga cikin mai magana da yawun kungiyar yakin neman zaben Tinubu-Shettima, ya ce mataimakin shugaban kasar ya yi kira ga wadanda abin ya shafa da su gudanar da ayyukansu ba tare da tsangwama ba.

Ya kuma bukaci jama’a da su yi watsi da duk wani bayani da ke nuna akasin haka.

A cikin wani sakon twitter, ya rubuta: “Dole ne a lura cewa a wani taro a yau, H.E. VP @ProfOsinbajo ya ƙarfafa duk ma’aikatan OVP – waɗanda ke da gata a nada su a cikin @officialABAT 2023 Majalisar Yakin Neman Zabe – don ba da mafi kyawun su ga muhimmin ƙoƙarin ba tare da tsangwama ba. Yi watsi da duk wani abu da aka saba. ”

A kwanakin baya ne jam’iyyar APC ta fitar da jerin sunayen ‘yan majalisar yakin neman zaben ta

Jerin sunayen majalisar, wanda ya kunshi mambobi 422, Sakataren PCC, James Faleke, dan majalisar tarayya ne ya fitar da shi.

An dai ce an samu sabani tsakanin Osinbajo da Tinubu ne biyo bayan matakin da mataimakin shugaban kasar ya dauka na tsayawa takarar shugaban kasa.

Daga nan sai aka yiwa mataimakin shugaban kasar lakabin maci amana saboda ya zabi tsayawa takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC tare da Tinubu, wanda ake kyautata zaton uban gidan sa ne na siyasa.

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp