fidelitybank

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Date:

Ma’aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution Company (AEDC), sun yi barazanar tsunduma yajin aiki saboda abin da suka ce rashin biya musu buƙatunsu.

Kamfanin na AEDC na samar wa Abuja babban birnin Najeriya wuta, da kuma jihohin Nasarawa da Kogi da Neja masu maƙwabtaka.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito wata wasiƙa da ƙungiyoyin ma’aikatan biyu suka aike wa mahukuntan kamfanin domin sanar da su aniyarsu, suna masu cewa “yajin aikin zai iya farawa a kowane lokaci”.

“Ku tuna cewa mun ƙulla yarjejeniya da ku a ranar 27 ga watan Satumban 2024 domin jingine yajin aiki game da rikicin kasuwanci da suka shafi ma’aikata,” kamar yadda jaridar ta ambato wasiƙar na bayyanawa.

“Muna tunasar da ku matsalar ƙin biyan fanshonmu da aka cire mana tsawon wata 16, da ƙin fara biyanmu sabon mafi ƙarancin albashi, da ƙin ƙara wa ma’aikata matsayi tsawon shekara 10, da ƙin tabbatar da ma’aikata na wucin gadi a matsayin cikakku.”

legit news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp