Ma’aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution Company (AEDC), sun yi barazanar tsunduma yajin aiki saboda abin da suka ce rashin biya musu buƙatunsu.
Kamfanin na AEDC na samar wa Abuja babban birnin Najeriya wuta, da kuma jihohin Nasarawa da Kogi da Neja masu maƙwabtaka.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito wata wasiƙa da ƙungiyoyin ma’aikatan biyu suka aike wa mahukuntan kamfanin domin sanar da su aniyarsu, suna masu cewa “yajin aikin zai iya farawa a kowane lokaci”.
“Ku tuna cewa mun ƙulla yarjejeniya da ku a ranar 27 ga watan Satumban 2024 domin jingine yajin aiki game da rikicin kasuwanci da suka shafi ma’aikata,” kamar yadda jaridar ta ambato wasiƙar na bayyanawa.
“Muna tunasar da ku matsalar ƙin biyan fanshonmu da aka cire mana tsawon wata 16, da ƙin fara biyanmu sabon mafi ƙarancin albashi, da ƙin ƙara wa ma’aikata matsayi tsawon shekara 10, da ƙin tabbatar da ma’aikata na wucin gadi a matsayin cikakku.”