fidelitybank

Ma’aikatan kananan masana’antu sun yi zanga-zanga a kan karin wuta a Kano

Date:

Ma’aikatan kananan masana’antu, SMEs a karamar hukumar Nasarawa ta jihar Kano, sun gudanar da zanga-zangar nuna adawa da karin kudin wutar lantarki, inda suka bayyana hakan a matsayin barazana ga ayyukansu.

A cewarsu, da yawa daga cikin SMEs na shirin rufe ayyukan saboda karin kudin wutar lantarki.

Aisha Abdullahi, wacce ta yi magana a madadin mata masu zanga-zangar, ta bayyana cewa ana kai musu farmaki, inda ta jaddada cewa ma’aikatan SMEs na shirin rufe ayyukan saboda ba za su iya biyan sabon kudin harajin ba.

Ta ce, “Ba mu da komai sai wannan aikin. Ba mu nemi aikin gwamnati a ko’ina ba. Muna nan muna gudanar da ƴan kuɗi kaɗan don raya jiki da rai. Abin takaici, za a fitar da mu waje.

“Kwanaki biyar kenan ba mu yi aiki ba, kuma Allah ne kadai ya san abin da zai faru idan kamfanonin SMEs suka yanke shawarar rufewa gaba daya saboda karin kudin wutar lantarki. Muna rokon hukumomin da abin ya shafa su sake duba wannan karin.”

Daya daga cikin masu gudanar da SME a yankin, Alhaji Isma’ila Shehu Dakata, ya ce karin kudin fiton ba shi da fuskar dan Adam domin ya zarce abin da yawancin kamfanoni ke iya samu.

Sai dai wakilin gwamnatin jihar Kano a yankin, Alhaji Zilkifilu Alhassan, ya bada tabbacin cewa zai tabbatar da cewa gwamnatin jihar ta shiga cikin lamarin, inda ya roki kamfanonin da kada su rufe.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp