fidelitybank

Ma’aikatan INEC a Kano sun koka a kan kudin aikin su

Date:

Wata matsala da ake fuskanta a jihar Kano, ita ce ta rashin biyan ma’aikatan INEC na wucin gadi kuɗaɗensu na alawus.

Wani da BBC ta zanta da shi ya ce tun daga lokacin da suka fara karɓar horo kan wannan aikin, ba a basu komi ba, kuma sai da suka kwashe kwana biyu suna barci a kan benci.

“Kwana na ɗaya da yini guda ban ci komi ba, babu wanda ya kawo mana ko da ruwan sha balle maganar kuɗin mota, kuɗi muka ara muka zo nan.

“Da muka zo nan an faɗa mana ana bayar da alawus na dubu huɗu amma a yanzu cikin ƙasa da awa guda an ce wai an koma bayar da 3,500, an rage ɗari biyar,” in ji wani ma’aikaci da BBC ta zanta da shi.

Karanta Wannan: Da Dumi-Dumi: An kona ofishin INEC na Takai a Kano

Duk da cewa sunayensu na cikin jerin waɗanda za su yi zaɓen gwamna, amma ya ce shi ba zai yi wannan aiki ba a lokacin zaɓen gwamna mai zuwa.

Sai dai, mun tuntuɓi jami’ar hulɗa da jama’a ta hukumar INEC Zainab Aminu Abubakar domin ji daga gareta, inda ta ce bata da matsaniyar wannan magana, amma ta ce za su yi bincike kan lamarin.

vanguard news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...
X whatsapp