Wata matsala da ake fuskanta a jihar Kano, ita ce ta rashin biyan ma’aikatan INEC na wucin gadi kuɗaɗensu na alawus.
Wani da BBC ta zanta da shi ya ce tun daga lokacin da suka fara karɓar horo kan wannan aikin, ba a basu komi ba, kuma sai da suka kwashe kwana biyu suna barci a kan benci.
“Kwana na ɗaya da yini guda ban ci komi ba, babu wanda ya kawo mana ko da ruwan sha balle maganar kuɗin mota, kuɗi muka ara muka zo nan.
“Da muka zo nan an faɗa mana ana bayar da alawus na dubu huɗu amma a yanzu cikin ƙasa da awa guda an ce wai an koma bayar da 3,500, an rage ɗari biyar,” in ji wani ma’aikaci da BBC ta zanta da shi.
Karanta Wannan: Da Dumi-Dumi: An kona ofishin INEC na Takai a Kano
Duk da cewa sunayensu na cikin jerin waɗanda za su yi zaɓen gwamna, amma ya ce shi ba zai yi wannan aiki ba a lokacin zaɓen gwamna mai zuwa.
Sai dai, mun tuntuɓi jami’ar hulɗa da jama’a ta hukumar INEC Zainab Aminu Abubakar domin ji daga gareta, inda ta ce bata da matsaniyar wannan magana, amma ta ce za su yi bincike kan lamarin.