Ma’aikatan hukumar kula da yanayi ta ƙasa Nimet, sun rufe ofishinsu na filin jirgin sama na Malam Aminu Kano.
Ma’aikatan sun ce sun shiga yajin aikin sai abin da hali ya yi ne saboda rashin kyakkyawan albashi, da rashin horo, da kuma ƙin biyansu haƙƙoƙinsu.
A safiyar yau Alhamis ne ma’aikatan hukumar suka jawo soke tashin wasu jirage saboda yajin aikin, inda kamfanin Air Peace ya sanar da dakatar da aiki.
Amma rahotonni sun ce wasu kamfanonin sun gudanar da jigilar a wasu filayen jirgin.