fidelitybank

Ma’aikatan asibitin jami’ar Oyo sun dakatar da aikin dare sakamakon rashin wuta

Date:

Ma’aikatan Asibitin Kwalejin Jami’ar UCH, Ibadan a Jihar Oyo sun dakatar da duk wani aikin dare.

Ma’aikatan sun ce sun fara gudanar da aikin da suka bayyana a matsayin raguwar ma’aikata, wanda ke nufin za su rika aiki ne daga karfe 8:00 na safe zuwa karfe 4:00 na yamma kowace rana.

Sun ce za su ci gaba da aiki daga karfe 8 na safe zuwa 4 na yamma har sai an dawo da wutar lantarki a asibiti.

Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na Ibadan, IBEDC, a ranar Talata, 19 ga Maris, 2024 ya katse UCH daga layin kasa.

Kamfanin rarraba wutar lantarki a wata sanarwa da ya fitar ya yi ikirarin cewa ya katse wa UCH wutar lantarki saboda bashin N495m.

Ma’aikatan asibitin, sun ce sun dakatar da duk wasu ayyukan dare ba tare da bata lokaci ba.

Shugaban kwamatin hadin gwiwa na kungiyar kwadagon da ke asibitin, Oludayo Olabampe, a lokacin da yake zantawa da DAILY POST a ranar Laraba, ya bayyana cewa ma’aikatan sun dauki matakin ne saboda rashin wutar lantarki a asibitin.

Olabampe ya sanar da cewa babu wanda zai samu halartar marasa lafiya da yamma.

Olabampe ya ce, “Har yanzu, haske bai dawo ba. Don haka, mun rage ayyukanmu. Za mu yi aiki tsakanin 8.am da 4.pm kowace rana.

“Mun ce idan har ba a dawo da hasken ba kamar jiya, za mu rage ayyukanmu kuma mun yi hakan tun jiya.

“Wannan shine na baya-bayan nan. Yanzu muna cikin mako na uku”.

world news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp