Shugaba Cyril Ramaphosa na Afirka ta Kudu, ya fice daga taron gangamin ranar ma’aikata ta duniya, bayan da ma’aikata suka mamaye dandalin da yake jawabi tare da yi masa ihun bama yi.
Suna rera wake cewar, “Cyril dole ya tafi,” sun daga alamun neman karin albashi a lokacin wani biki a wani filin wasa kusa da birnin Rustenburg da ke arewa maso yammacin kasar.
Masu zanga-zangar, wadanda ke aiki a wata mahakar ma’adinai, sun shafe makonni suna zanga-zangar.
Shugaba Ramaphosa ya yi kokarin magance damuwar masu hakar ma’adinan, amma sai suka yi ta ihu.
Ma’aikatan na son a kara albashin rand 1,000 na shekara-shekara ($ 63; £50). bukatar da shugaba Ramaphosa ya yi jawabi kai tsaye.