fidelitybank

Ma’aikata fararen hula sun yi wa sojoji zanga-zanga

Date:

Ma’ikata fararen hula da ke aiki a cibiyoyin ma’aikatun tsaron sojoji a kasar nan, sun gudanar da wata zanga-zanga tare da rufe ma’aikatar tsaron sojoji da ke Abuja.

Ma’aikatan dai sun gudanar da wannan zanga-zangar ne bisa zargin da suke cewa sojoji na cin zarafin su, inda da dama daga cikin su ke ci gaba da zama a tsare a hannun sojoji.

Sun bayyana cewa, jami’an sojoji na ƙuntata musu ta hanyar dukan su da kuma kulle su a gadirum, duk da cewa su fararen hula ne ba sojoji ba.

Masu zanga-zangar sun kuma bayar da misali da wani mai suna Ambrose Akhigbe, wanda mataimakin darakta ne a makarantar sakandiren ‘ya’yan sojoji da ke jihar Legas da wani jami’in soji ya azabtar da shi a ranar Litinin ba tare da la’akari da dokokin da suka shafi ma’aikatan gwamnati fararen hula ba.

Bayan aukuwar wannan zanga-zanga ta wadannan ma’aikatan, Dakta Ibrahim Abubakar Kana babban sakatare a ma’aikatar tsaro ta kasa ya yi wa ma’akatan jawabi, cewa za a duba korafi na su.

Ya kuma ce an kama dukan wadanda ake zargi da hannu a cin zarafin ma’aikata fararen hulha da ke cibiyoyin tsaron.

An dade ana bayyana cewa jami’na sojoji na yi wa ma’aikta fararen hular gwale-gwale tare irin na sojojin, a duk lokacin da wani abu ya faru tsakaninsu, sai dai wannan shi ne kusan karo na farko da aka samu sun fito sun bayyana damuwarsu a fili.

besda

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp