‘Yan Sandan kasar Brazil, sun cafke wani mutum da ake zargin ya shiga asusun mutane ya sace musu kudade ciki har da dan wasa Neymar.
Wani ma’aikacin banki ne ake tuhuma da laifin sace Dala dubu 40, 000 daga akawun din ‘Dan wasa Neymar, duk da bai san an dauki wannan kudi daga asusun sa ba, sai daga baya ya sanar da hukuma.
A sanarwar da ‘yan sanda suka fitar a birnin Sao Paulo, ta ce, mai kutse ya na aiki ne a wani banki da ba a ambaci sunansa ba, da Neymar da mahaifinsa suke ajiyar kudaden su.