fidelitybank

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Date:

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool kan fam miliyan 65.5.

Ɗan ƙwallon tawagar Colombia ya saka hannu kan yarjejeniyar kaka huɗu da ƙungiyar Jamus, hakan ya kawo karshen shekara uku da rabi da ya yi a Liverpool.

Mai shekara 28 ya bar sansanin Liverpool a nahiyar Asia lokacin da za ta kara da AC Milan ranar Asabar, saboda jita-jitar da ta yi yawa kan makomar ɗan wasan a Anfield.

Tun farko Liverpool ba ta amince da tayin fam miliyan 58.6 da Bayern ta fara yi ba, hakan ya sa aka kara kuɗin sayen Diaz daga baya ƙungiyar Anfield ta amince ta kuma yadda yaje Jamus aka auna koshin lafiyarsa.

Diaz ya koma Liverpool daga Porto kan fam miliyan 37 a Janairun 2022, ya ci ƙwallo 41 a wasa 148 a ƙungiyar Anfield.

Ya lashe FA Cup da League Cup a kakarsa ta farko a Liverpool, yana cikin ƴan wasan da suka yi rashin nasara a hannun Real Madrid a Champions League a 2022.

Diaz ya taka rawar gani a kakar da ta wuce a babbar gasar tamaula ta Ingila, wanda ya ci ƙwallo 17 da ɗaukar kofin Premier League.

Tafiyar da Diaz ya yi, Liverpool ta sayar da ƴan wasa kan fam miliyan 115 a bana.

Ta kuma sayi ƴanwasa kan fam miliyan 270 da ya haɗa da Florian Wirtz da Hugo Ekitike da Jeremie Frimpong da kuma Milos Kerkez.

Har yanzu Liverpool na son yin zawarcin ɗan ƙwallon Newcastle, Alexander Isak, wanda bai bi ƙungiyarsa wasannin atisaye da take yi a nahiyar Asia ba.

 

naija news today legits

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...

Ba za mu jingine yajin aiki ba har sai an biya mana buƙatun mu – Ma’aikatan Jinya

Shugaban ƙungiyar ma'aikatan jinya ta Najeriya, Morakinyo-Olajide Rilwan ya...

Za a fara yi wa Dalibai gwajin kwaya kafin su shiga jami’a – NDLEA

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta fara yi wa...

Za mu kammala titin jirgi na Kaduna zuwa Kano a 2026 – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya, ta ce za a kammala aikin titin...

Adadin kudaden da Liverpool ta kashe wajen daukar ‘yan wasa

Liverpool ta kashe fam miliyan 265 wajen ɗauko ƴanƙwallon...

Sunderland ta ɗauko ƴanƙwallo bakwai a kakar bana

Granit Xhaka ya zaman ɗan ƙwallo na bakwai da...

James Trafford ya sake komawa Man City daga Burnley

Mai tsaron ragar tawagar Ingila, mai shekara 21, James...

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool...

NNPCL ya musanta sayar da matatar mai ta Fatakwal

Babban kamfanin man fetur na kasa, NNPCL ya musanta...
X whatsapp