fidelitybank

Luiz Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool

Date:

Luis Diaz ya kammala komawa Bayern Munich daga Liverpool kan fam miliyan 65.5.

Ɗan ƙwallon tawagar Colombia ya saka hannu kan yarjejeniyar kaka huɗu da ƙungiyar Jamus, hakan ya kawo karshen shekara uku da rabi da ya yi a Liverpool.

Mai shekara 28 ya bar sansanin Liverpool a nahiyar Asia lokacin da za ta kara da AC Milan ranar Asabar, saboda jita-jitar da ta yi yawa kan makomar ɗan wasan a Anfield.

Tun farko Liverpool ba ta amince da tayin fam miliyan 58.6 da Bayern ta fara yi ba, hakan ya sa aka kara kuɗin sayen Diaz daga baya ƙungiyar Anfield ta amince ta kuma yadda yaje Jamus aka auna koshin lafiyarsa.

Diaz ya koma Liverpool daga Porto kan fam miliyan 37 a Janairun 2022, ya ci ƙwallo 41 a wasa 148 a ƙungiyar Anfield.

Ya lashe FA Cup da League Cup a kakarsa ta farko a Liverpool, yana cikin ƴan wasan da suka yi rashin nasara a hannun Real Madrid a Champions League a 2022.

Diaz ya taka rawar gani a kakar da ta wuce a babbar gasar tamaula ta Ingila, wanda ya ci ƙwallo 17 da ɗaukar kofin Premier League.

Tafiyar da Diaz ya yi, Liverpool ta sayar da ƴan wasa kan fam miliyan 115 a bana.

Ta kuma sayi ƴanwasa kan fam miliyan 270 da ya haɗa da Florian Wirtz da Hugo Ekitike da Jeremie Frimpong da kuma Milos Kerkez.

Har yanzu Liverpool na son yin zawarcin ɗan ƙwallon Newcastle, Alexander Isak, wanda bai bi ƙungiyarsa wasannin atisaye da take yi a nahiyar Asia ba.

 

bbc naija news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp