fidelitybank

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Date:

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan kasarsa Luis Díaz ya yi zabin da ya dace ya bar Liverpool zuwa Bayern Munich.

Ku tuna cewa kwanan nan Diaz ya bar Reds ya koma Bayern Munich a matsayin dindindin.

Dan wasan mai shekaru 28 ya fara buga wa zakarun na Bundesliga wasan sada zumuncin da suka doke Lyon da ci 2-1 a ranar Asabar.

Da yake magana kan komawar Díaz zuwa Bayern, Rodríguez, wanda kuma ya taba bugawa kungiyar ta Jamus a baya, ya ce dan wasan zai taimakawa kungiyar ta Vincent Kompany a wannan sabuwar kakar.

“Ina ganin Luis Díaz ya yi zabi mai kyau. Bayern ta sanya hannu kan babban dan wasa,” in ji Rodríguez ta hanyar The TouchlineX.

“Lucho ya dace da su, Bayern babbar kungiya ce, ina ganin zai taimaka musu sosai.”

Díaz zai yi fatan zai jagoranci Bayern zuwa nasara idan za su kara da Tottenham Hotspur a wasan sada zumunci a ranar Alhamis.

vanguard 
nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iya wa’adi daya ya ishe ni a mulkin Najeriya – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugabancin Najeriya a jam'iyyar Labour, Peter...

Luis Diaz ya zaba wa kansa makoma da ya bar Liverpool – James

Kyaftin din Colombia, James Rodríguez, ya dage cewa dan...

Ka fito ka baiwa Matawalle hakuri ko ka fuskanci fushin kotu – Shinkafi

Wani mai fafutukar kare hakkin bil’adama, Dakta Suleiman Shuaibu...

Liverpool za su sayar da ‘yan wasa uku su dauki Isak

Liverpool a shirye take ta sayar da matasan yan...

Ba zamu daga wa Hamas kafa ba har sai an saki mutanen mu – Netanyahu

Firaiministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce, ya yi dogon...

Za mu gyara tsarin Maiduguri saboda ambaliya – Zulum

Gwamnan jihar Borno Babagana Umara Zulum ya ce, gwamnatinsa...

Dubban mutane sun yi zanga-zangar goyon bayan Falasɗinawa a Australia

Dubban mutane ne suka gudanar da zanga-zangar goyon bayan...

Mata da kanan Yara ne Ambaliya ta daidaita a jihohi 19 – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa, NEMA, ta...

Facebook ya ƙi amincewa da tsare-tsaren Turai na amfani da AI

Wasu muhimman tsare-tsare na dokokin Tarayyar Turai kan amfani...

Ranar 18 za a fara rajistar zabe – INEC

Hukumar zaɓe mai zaman kanta, INEC ta sanar da...

Trump ya tura jiragen ruwa na yaki masu dauke da makaman nukiliya kusa da Rasha

Shugaba Trump ya ce, ya umarci a matsar da...

Amnesty na tuhumar gwamnatin Najeriya kan bacewar Dadiyata

Ƙungiyar Amnesty International ta yi Allah-wadai da sakacin da...
X whatsapp