Wani jami’in Hukumar Kula da ‘Yan Gudun Hijirar FalasÉ—inawa ta Majalisar Dinkin Duniya UNRWA, daga birnin Rafah na kudancin gaza, ya ce fararen hula cikin ‘mawuyacin hali’ a yankin.
Yayin da yake bayyana abin da ya gani a lokacin da ya je wata cibiyar rabon tallafi a Rafah ranar Juma’a, Tom White ya ce ”babu abin da ke kake ji a birnin sai Æ™arar hare-hare”.
Ya ce tsagaita wuta na da matuÆ™ar muhimmanci, domin kuwa a cewarsa ”a Rafah akwai É—aruruwan mutanen da ke kwana a waje, muna fuskantar Æ™arancin ruwan sha, duk wanda ka gani a gefen titi na neman abincin da zai bai wa ‘ya’yansa su ci”.
“Gidajenmu sun cika da mutane, za ka samu daruruwan mutane na amfani da ban É—aki guda É—aya”.
“In ma bom bai kashe su ba, to cutuka za su kashe su, saboda yadda mutane ke kwana a kan tituna.”
Ya kuma ce ya samu labarin cewa jiya da daddare an kai hari kan gidan da suka sauka a lokacin da suka je cibiyar.