Louis van Gaal ya sanar da cewa yana karbar maganin ciwon daji na prostate.
Da yake magana a wani shirin gidan talabijin na kasar Holland Humberto, babban kocin na Netherlands ya ce, ya dade yana fama da wannan matsalar kuma an yi masa magani sau 25.
Van Gaal, mai shekaru 70, ya jagoranci wasannin sada zumunci biyu na kasa da kasa da Netherlands a watan da ya gabata, inda tawagarsa ta doke Denmark da ci 4-2, sannan suka tashi 1-1 da Jamus.
Tsohon kociyan Manchester United, Barcelona, Bayern Munich da Ajax ya ce, ya boye wa ‘yan wasan sa cutar da ya yi, kuma ya bayyana cewa, an garzaya da shi asibiti domin yin jinya a lokacin hutun kasashen duniya.