An zabi Ademola Lookman a matsayin gwarzon dan wasan gaba na Serie A a cikin babbar lambar yabo ta Gran Gala del Calcio.
‘Yan wasan Inter Milan biyu, Lautaro Martinez da Marcus Thuram, da kuma Rafael Leao na AC Milan su ne sauran ‘yan wasan gaba da aka zaba don kyautar.
Kocin Atalanta, Gain Piero Gasperini shi ma yana cikin masu neman kyautar gwarzon koci na shekara.
Lookman ya taka rawar gani a Atalanta wannan kakar.
Dan wasan mai shekaru 27 ya zura kwallaye takwas sannan ya taimaka biyar a wasanni 14 da ya buga a duk gasa.
Dan Najeriya ya ci kwallaye 17 sannan ya taimaka 10 a duk wasannin da ya buga a La Dea a kakar wasan da ta wuce.
Dan wasan ya kare a matsayi na 14 a matsayin Ballon d’or na 2024.
Shi ne babban wanda aka fi so ya lashe kyautar gwarzon dan wasan CAF na shekarar 2024.