Ɗan takarar shugabancin kasa a Jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi kira ga Babban Bankin Kasa CBN da ya ƙara wa’adin daina karɓar tsofaffin kuɗin da aka sauya.
Cikin wani bidiyo da Atiku ya wallafa a shafukansa na sada zumunta, ɗan takarar shugaban ƙasar ya ce idan aka yi duba da halin matsi da al’umma ke ciki ya kamata a ƙara wa’adin zuwa wani ɗan lokaci.
A cewar Atiku sauya fasalin kuɗi ba wani sabon abu ba ne a fadin duniya, ka zalika matakin ba sabo ba ne ga Najeriya, sai dai wa’adin da aka tsayar na 31 ga watan Janairun da muke ciki na jefa mutane cikin mawuyacin hali.
“Da yawan ‘yan Najeriya musamman manoma da masu sana’ar hannu da mazauna ƙauyuka ba su da asusun banki, dan haka lokacin da aka ka’ide na daina karbar tsofaffin kuɗi ba mai yiwuwa ba ne,” in ji Atiku Abubakar.
‘Yan Najeriya da dama na ta kiraye-kirayen CBN ya sake nazari kan wannan wa’adi, la’akari da ƙarancin sabbin takardun kuɗin da ake da su a ƙasar.