fidelitybank

Lokacin sauya karbar kudi ba mai yuwa ba ne – Atiku

Date:

Ɗan takarar shugabancin kasa a Jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi kira ga Babban Bankin Kasa CBN da ya ƙara wa’adin daina karɓar tsofaffin kuɗin da aka sauya.

Cikin wani bidiyo da Atiku ya wallafa a shafukansa na sada zumunta, ɗan takarar shugaban ƙasar ya ce idan aka yi duba da halin matsi da al’umma ke ciki ya kamata a ƙara wa’adin zuwa wani ɗan lokaci.

A cewar Atiku sauya fasalin kuɗi ba wani sabon abu ba ne a fadin duniya, ka zalika matakin ba sabo ba ne ga Najeriya, sai dai wa’adin da aka tsayar na 31 ga watan Janairun da muke ciki na jefa mutane cikin mawuyacin hali.

“Da yawan ‘yan Najeriya musamman manoma da masu sana’ar hannu da mazauna ƙauyuka ba su da asusun banki, dan haka lokacin da aka ka’ide na daina karbar tsofaffin kuɗi ba mai yiwuwa ba ne,” in ji Atiku Abubakar.

‘Yan Najeriya da dama na ta kiraye-kirayen CBN ya sake nazari kan wannan wa’adi, la’akari da ƙarancin sabbin takardun kuɗin da ake da su a ƙasar.

bbc news nigeria today live

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp