fidelitybank

Lokacin sauya karbar kudi ba mai yuwa ba ne – Atiku

Date:

Ɗan takarar shugabancin kasa a Jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya yi kira ga Babban Bankin Kasa CBN da ya ƙara wa’adin daina karɓar tsofaffin kuɗin da aka sauya.

Cikin wani bidiyo da Atiku ya wallafa a shafukansa na sada zumunta, ɗan takarar shugaban ƙasar ya ce idan aka yi duba da halin matsi da al’umma ke ciki ya kamata a ƙara wa’adin zuwa wani ɗan lokaci.

A cewar Atiku sauya fasalin kuɗi ba wani sabon abu ba ne a fadin duniya, ka zalika matakin ba sabo ba ne ga Najeriya, sai dai wa’adin da aka tsayar na 31 ga watan Janairun da muke ciki na jefa mutane cikin mawuyacin hali.

“Da yawan ‘yan Najeriya musamman manoma da masu sana’ar hannu da mazauna ƙauyuka ba su da asusun banki, dan haka lokacin da aka ka’ide na daina karbar tsofaffin kuɗi ba mai yiwuwa ba ne,” in ji Atiku Abubakar.

‘Yan Najeriya da dama na ta kiraye-kirayen CBN ya sake nazari kan wannan wa’adi, la’akari da ƙarancin sabbin takardun kuɗin da ake da su a ƙasar.

latest news in lokoja, kogi state

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp