Joe Biden zai ziyarci Angola da Cape Verde a ziyararsa ta farko zuwa Afirka a matsayinsa na shugaban ƙasa.
A Luanda, ana sa ran zai bayyana lamuni da Amurka za ta bayar don taimakawa gina sabon layin dogo mai tsawon kilomita dubu ɗaya da ɗari uku.
Za ta hade tashar ruwan Lobito ta Angola da yankin da ake sarrafa jan ƙarfe (copper) na Zambia da kuma wuraren haƙar ma’adinan Cobalt na Jamhuriyar Demokradiyyar Kongo.
Ana kallon wannan aikin a matsayin wani ƙalubale ne ga mamayar da ƙasar China ke neman yi a fannin haƙar ma’adinai da ababen more rayuwa a yankin.
China ta rattaba hannu kan wata yarjejeniya da ƙasashen Tanzania da Zambia a watan Satumba domin farfaɗo da layin dogo da ke yankin gabashin Afirka.