fidelitybank

Lokaci ya yi da ƴan Najeriya za su fara gani a ƙasa

Date:

Ministan kula da dabbobi na Najeriya, Alhajij Idi Mukhtar Maiha, ya ce ya kamata ƴan Najeriya su fara gajiya da maganar cewa ƙasar na da damarmaki, inda a cewarsa, lokaci ya yi za ya kamata su fara a gani a ƙasa.

Maiha ya bayyana haka a taron tattaunawa wanda jaridar Daily Trust ta shirya na bana, wanda shi ne karo na 22, inda ya ce ya kamata tsare-tsaren harkokin noma su kawo hanyoyin da za a kawo sauyi kan yadda manoma suke noma kawai domin su ci, sai kaɗan suke sayarwa.

Ya ce akwai buƙatar a canja yadda ake kallon harkokin noma da kiwo a ƙasar, sannan ya ƙara da cewa ma’aikatarsa za ta inganta harkokin kiwo.

Sai dai ya ce matsalar rashin tsaro ta shafi harkokin samar da abinci a ƙasar, sannan ya yi kira da rumgumi harkokin noma a damuna da rani, wanda a cewarsa hakan ne kawai zai magance ƙarancin abincin, sannan ya rage farashinsa.

A ƙarshe ya yi kira da a magance matsalar rikice-rikicen manoma da makiyaya, inda ya ce ma’aikatansa na aiki tuƙuru domin magance matsalar.

Tun da farko, shugaban kamfanin Media Trust, Malam Kabiru Yusuf ya ce alƙaluma suna nuna cewa akwai damuwa a ɓangaren samar da abinci a ƙasar.

A jawabinsa a wurin taron mai taken: Samar da abinci: Samar da shi da farashi, ya ce “me ya sa ƴan Najeriya suke shan wahalar samun isasshen abinci? dole mu duba batun nan, muna jira mu ji me masana za su ce game da samar da abincin da farashinsa.”

tribune news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...

Iran ta zartar da hukuncin kisa a kan Mutane 3

Hukumomi a Iran sun zartar wa mutum uku hukuncin...

Ƴansanda sun kama ƙasurgumin ɗanbindiga a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna ta ce, jami'an ta sun...

Sudan ta Kudu ta yi ta’aziyyar Buhari

Mukaddashin Ministan Harkokin Wajen Sudan ta Kudu, Ambasada Akuei...

Trump ya na fama da cuta mai kumbura kafa da toshewar hanyar jini

A ranar Alhamis ne Fadar White House ta sanar...

Yadda aka gudanar da addu’o’in Buhari a Villa

A ranar Alhamis ne aka gudanar da addu'o'i ga...
X whatsapp