fidelitybank

Lokaci ya yi da za mu hukunta ‘yan siyasa masu ci da addini – EL-Rufa’i

Date:

Gwamnan jihar Kaduna, Mallam Nasir El-Rufai, ya ce, lokaci ya yi da za a cire batun addini daga siyasar ƙasa tare da hukunta ‘yan siyasar da ke amfani da addini a matsayin makamin yaƙin neman zaɓe.

Rahotonni sun ambato gwaman na wannan maganar ranar Talata a lokacin bikin ƙaddamar da babban ofishin ‘gidauniyar zaman lafiya da ci gaba’ ta mai alfarma sarkin musulmi

El-Rufai ya yi kira ga Sarakunan gargajiya da malaman addini da su riƙa gudanar da addu’o’in samun ingantaccen zaɓe da samun zaman lafiya a fadin ƙasar.

Ya ce “Ina so na yi amfani da wannan damar na yi kira ga shugabanninmu da ke nan, masu girma sarakunan gargajiya da malamanmu da su ci gaba da yi wa ƙasarmu addu’o’in samun zaman lafiya da samun ingantaccen zaɓe, tare da yin addu’ar Allah ya zaɓa wa ƙasarmu shugabannin na-gari da za su haɗa kan ƙasar tare da ciyar da ita gaba”

”A matsayina na ɗan ƙasa, kuma gwamna sannan kuma musulmi bana jin daɗin yadda wasu ‘yan siyasa ke amfani da addini da ƙabilanci a matsayin makaminsu na yaƙin neman zaɓe”, in ji El-Rufai.

Haka kuma gwamnan ya ce lokaci ya yi da za a cire batun addini daga siyasar ƙasar tare da hukunta waɗanda ke ƙoƙarin amfani da addinin a matsayin makamin yaƙin neman zabe.

vgn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...

An fara binciken fashewar wani abu da ya kashe mutane 5 da jikkata da dama a Kano

Wani abin fashewa da ake tunanin bom ne ya...

An samu fashewar wani abu a kamfanin ƴan Chana a Kano

An samu fashewar wani abu a Kamfanin Ƙarfe na...

Ma’aikacin kamfani ya kashe abokin aikinsa a Kano

Rahoton da ke yawo a kafafen sada zumunta ya...

Kotu ta ɗaure Matashin da yake tare titi a Kano da sunan barƙwanci

Kotun majistire da ke unguwar Nomansland a Kano, karkashin...

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...
X whatsapp