fidelitybank

Lokaci ya yi da ƴan Najeriya za su fara gani a ƙasa

Date:

Ministan kula da dabbobi na Najeriya, Alhajij Idi Mukhtar Maiha, ya ce ya kamata ƴan Najeriya su fara gajiya da maganar cewa ƙasar na da damarmaki, inda a cewarsa, lokaci ya yi za ya kamata su fara a gani a ƙasa.

Maiha ya bayyana haka a taron tattaunawa wanda jaridar Daily Trust ta shirya na bana, wanda shi ne karo na 22, inda ya ce ya kamata tsare-tsaren harkokin noma su kawo hanyoyin da za a kawo sauyi kan yadda manoma suke noma kawai domin su ci, sai kaɗan suke sayarwa.

Ya ce akwai buƙatar a canja yadda ake kallon harkokin noma da kiwo a ƙasar, sannan ya ƙara da cewa ma’aikatarsa za ta inganta harkokin kiwo.

Sai dai ya ce matsalar rashin tsaro ta shafi harkokin samar da abinci a ƙasar, sannan ya yi kira da rumgumi harkokin noma a damuna da rani, wanda a cewarsa hakan ne kawai zai magance ƙarancin abincin, sannan ya rage farashinsa.

A ƙarshe ya yi kira da a magance matsalar rikice-rikicen manoma da makiyaya, inda ya ce ma’aikatansa na aiki tuƙuru domin magance matsalar.

Tun da farko, shugaban kamfanin Media Trust, Malam Kabiru Yusuf ya ce alƙaluma suna nuna cewa akwai damuwa a ɓangaren samar da abinci a ƙasar.

A jawabinsa a wurin taron mai taken: Samar da abinci: Samar da shi da farashi, ya ce “me ya sa ƴan Najeriya suke shan wahalar samun isasshen abinci? dole mu duba batun nan, muna jira mu ji me masana za su ce game da samar da abincin da farashinsa.”

sun news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp