Ministan kula da dabbobi na Najeriya, Alhajij Idi Mukhtar Maiha, ya ce ya kamata ƴan Najeriya su fara gajiya da maganar cewa ƙasar na da damarmaki, inda a cewarsa, lokaci ya yi za ya kamata su fara a gani a ƙasa.
Maiha ya bayyana haka a taron tattaunawa wanda jaridar Daily Trust ta shirya na bana, wanda shi ne karo na 22, inda ya ce ya kamata tsare-tsaren harkokin noma su kawo hanyoyin da za a kawo sauyi kan yadda manoma suke noma kawai domin su ci, sai kaɗan suke sayarwa.
Ya ce akwai buƙatar a canja yadda ake kallon harkokin noma da kiwo a ƙasar, sannan ya ƙara da cewa ma’aikatarsa za ta inganta harkokin kiwo.
Sai dai ya ce matsalar rashin tsaro ta shafi harkokin samar da abinci a ƙasar, sannan ya yi kira da rumgumi harkokin noma a damuna da rani, wanda a cewarsa hakan ne kawai zai magance ƙarancin abincin, sannan ya rage farashinsa.
A ƙarshe ya yi kira da a magance matsalar rikice-rikicen manoma da makiyaya, inda ya ce ma’aikatansa na aiki tuƙuru domin magance matsalar.
Tun da farko, shugaban kamfanin Media Trust, Malam Kabiru Yusuf ya ce alƙaluma suna nuna cewa akwai damuwa a ɓangaren samar da abinci a ƙasar.
A jawabinsa a wurin taron mai taken: Samar da abinci: Samar da shi da farashi, ya ce “me ya sa ƴan Najeriya suke shan wahalar samun isasshen abinci? dole mu duba batun nan, muna jira mu ji me masana za su ce game da samar da abincin da farashinsa.”