Gwamnan jihar Ekiti, Dr Kayode Fayemi a ranar Larabar da ta gabata ya bayyana cewa ba zai yi wani shela a bainar jama’a ba don tsayawa takarar shugaban kasa a zaben 2023 a karkashin jam’iyyar APC har sai an kammala Azumin Ramadan.
Gwamna Fayemi ya bayyana haka ne a jihar Gombe a lokacin da ya kai wa Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya ziyara.
Fayemi wanda shi ne Shugaban Kungiyar Gwamnonin Najeriya (NGF) ya ce, tuni ya dauki matsaya kan ko zai tsaya takarar Shugaban kasa a 2023 ko a’a.
Sai dai ya bayyana cewa, lokaci bai yi ba don bayyana matsayar sa ga ‘yan Najeriya.
Ya bayyana cewa, kasar nan tana cikin yanayi na ibada, kuma ga ‘yan Najeriya, wadanda suke gudanar da Azumin watan Ramadan da Azumi, lokaci bai yi ba da zai yi shelar siyasa.