fidelitybank

Liman ya yi addu’a a kan barawon da ya sace masa ragon Sallah

Date:

Babban limamin unguwar Mista Ali da ke karamar hukumar Bassa a jihar Filato, Imam Abdulkadir ya koka a kan satar ragon da aka yi masa.

Lamarin ya faru ne a lokacin da aka yi ruwan sama kamar da bakin kwarya a yankin a jajibirin Ed-el-Kabir.

Wani Limamin Al’ummar garin Malam Haruna Yaqub ne ya bayyana haka a lokacin wa’azin bayan Sallar Raka’a biyu, inda ya yi Allah-wadai da wannan aika-aika tare da bayyana shi a matsayin rashin hankali.
“Ragon Babban Limaminmu, wanda da gangan ya saya domin ya yanka, an sace shi da dare.

“A gaskiya mun kadu matuka da lamarin. Mun yi mamakin jin wannan labari.

“Wannan yana nufin mutane ba sa tsoron Allah. Abin ban tsoro ne a ce mutane sun kai ga satar ragon da ake nufi da ayyukan addini,” inji Yaqub.

Yakub ya kuma bukaci jama’a da su ji tsoron Allah su nisanta kansu daga sata ko duk wata muguwar dabi’a, yana mai jaddada cewa kowa zai amsa abin da ya aikata a duniya da lahira.
Ya ce: “Lokaci ya yi da mutane za su tuba kuma su ɗauki tafarkin Allah. Ba a makara ba. Ya kamata mutane su daina aikata munanan abubuwa kuma su yi aiki da dokokin Allah.

kano news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp