Limamin cocin Katolika na Diocese Zaria a jihar Kaduna, Rabaran George Dodo ya mutu.
Dodo, wanda shi ne babban Bishop na cocin, an ce ya rasu ne da sanyin safiyar Juma’a bayan gajeriyar rashin lafiya.
Mataimakin shugaban Diocesan na Zaria, Rev Fr Abrahaman Bisan Make, ya sanar da rasuwar malamin a wata sanarwa da ya fitar a Kaduna ranar Juma’a.
Sanarwar ta umurci kowa da kowa ya yi addu’a don “lafiya” yayin da ta kara da cewa za a sanar da bayanan game da binne shi “da wuri-wuri”.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “Tare da godiya ga Allah, an umurce ni da in sanar da mutuwar Bishop din mu, Most Rev George Dodo, babban bishop na darikar Katolika na Zariya.
“Wannan abin bakin ciki ya faru ne da sanyin safiyar Juma’a, 7 ga Yuli, 2022, bayan gajeriyar rashin lafiya.”