fidelitybank

Likitoci sun janye yajin aikin kwanaki 17 da suka gudanar a Najeriya

Date:

Ƙungiyar lokitoci masu neman ƙwarewa a Najeriya ta janye yajin aikin da ta shiga bayan kwana 17, inda likitocin za su ci gaba da aiki daga yau Asabar.

Shugaban ƙungiyar National Association of Resident Doctors (NARD), Dr. Emeka Orji, ya faɗa wa BBC cewa sun jingine yajin ne bayan gwamnatin tarayya ta amince da kafa gidauniyar horaswa ta Medical Residency Training Fund.

Ya ƙara da cewa gwamnatin ta fara shirin biyan su alawus na rage wahalar aikin da suke sha a asibitocin gwamnati sakamakon ficewar likitoci zuwa ƙasashen waje, kamar yadda suka nema.

A cewar Dr. Orji, waɗannan ne manya daga cikin buƙatun nasu kuma za su zauna don duba cigaban da aka samu nan da mako biyu.

Likitocin waɗanda su ne kashi 60 cikin 100 na kafatanin likitocin gwamnati a Najeriya, sun ƙaurace wa ayyuka ranar 26 ga watan Yuli, suna masu neman ƙarin kulawa da kuma inganta yanayin aikin nasu.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama ɗan kasar China da zargin kai wa ƴan Boko Haram kayayyaki

Rundunar sojojin ƙasar nan ta kama wani dan kasar...

Isra’ila ta tsokano tsuliyar Dodo – Iran

Jagoran addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya ce...

Da sani na Isra’ila ta kai hari Iran – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump ya bayyana cewa, yana sane...

Farashin man fetur ya tashi bayan Isra’ila ta kai wa Iran hari

Farashin man fetur a kasuwannin duniya ya tashi bayan...

Isra’ila ta kashe manyan Jami’an tsaron Iran su biyar

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

Isra’ila ta kashe Manyan Jami’an Iran biyar a hare-hare

Wani hari da Isra'ila ta kira ‘Operation Rising Lion’,...

A dawo da tallafin aikin Hajji ga maniyyatan Najeriya – Ndume

Jagoran ƴan kwamitin majalisar dattijawa kan harkokin ƙasashen waje...

A na fargabar mutuwar dukkanin fasinjojin jirgin Indiya da ya yi hatsari

Kamfanin dillancin labaru na AP ya rawaito cewa, shugaban...

An kwashe wasu daga cikin Gawarwakin da Jirgi ya fada cikin gidaje a Indiya

Ƙungiyar likitoci ta ƙasar Indiya (FAIMA), ta ce an...

Tinubu ya mayar da martani kan mayar da Najeriya tsarin jam’iyya daya

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya mayar da martani game...

Zan cigaba da sa yawan jini ga maƙiya Tinubu – Wike

Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, ya sha alwashin...

Tinubu zai magantu a kan ranar Dimokradiyya

Shugaban Kasa, Bola Ahmed Tinubu, zai yi jawabi ga...
X whatsapp