Kungiyar likitoci masu neman kwarewa ta janye yajin aikin gargadi na kwana uku da mambobinta suka shiga a Abuja, babban birnin tarayyar Najeriya.
A wata sanarwa da shugaban kungiyar, Dr. George Ebong ya fitar a jiya Juma’a ya ce sun dakatar da yajin aikin ne bayan da ministan babban birnin Nyesome Wike ya shiga tsakani, inda aka biya musu da dama daga cikin bukatunsu.
A ranar Laraba ne kungiyar ta tsunduma yajin aikin a kan rashin biya musu wasu bukatu da suka hada da bashin albashi da kuma kudaden alawus-alawus da sauransu.
A sanarwar janye yajin aikin, dr Ebong ya ce tuni wasu daga cikin likitocin suka fara samun kudaden bashin da suke bi na karin albashi da ba a biya su ba na wata shida,
Shugaban ya ce bayan da ministan ya sa baki a kan bukatun nasu har aka fara share musu hawaye, likitocin sun koma bakin aiki a yau Asabar 25 ga watan Janairu, 2025.