fidelitybank

Likitoci sun hana Yarima mai jiron gadon Saudiyya doguwar tafiya

Date:

Tawagar likitocin Yarima mai jiran gadon Saudiyya sun shawarce shi da kar ya yi doguwar tafiya a jirgi saboda kauce wa matsalar kunne da doguwar tafiya a jirgi ke haddasawa.

Hakan na zuwa ne bayan da mahaifinsa Sarki Salman ya umarce shi da ya jagoranci tawagar kasar zuwa taron kolin kasashen Larabawa da Aljeriya ke karbar baƙunci.

Kamfanin dillancin labarai na AP ya ruwaito cewa likitocin masarautar ne suka fitar da sanarwar da kuma shawara ga Yariman ya dakatar da yin balaguron.

A don haka Sarki Salman ya umarci Ministan Harkokin Waje Yarima Faisal bin Farhan, ya wakilci kasar a madadin Yarima Muhammad.

Likitocin sun hana Yarima mai jiran gadon yin tafiya mai nisa a jirgi ne, “matukar ba za a tsaya wata kasa a huta ba, domin kaucewa matsalar kunne da doguwar tafiya a jirgi ke haddasawa, sakamakon tafiyar zuwa da dawowa ta kai tsawon awa 24.”

Sarki Salman ya ce, kasar Saudiya na tare da Aljeriya a kowanne hali, tare da nanata goyon baya ga duk matsayar da za a cimma a taron kolin.

Ranar 1-2 ga watan Nuwamba za a fara taron da za kasashe 31 na yankin gabas ta tsakiya za su halarta.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp