Kungiyar likitocin ƙasa reshen jihar Nasarawa, ta dakatar da yajin aikin gargaɗi na kwanaki biyar, inda ta bai wa gwamnatin jihar wa’adin makonni biyu da ta biya musu dukkan bukatunsu.
Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa kungiyar ta tsunduma yajin aikin ne bayan gazawar gwamnatin jihar wajen aiwatar da ƙarin matsayi ga wasu mambobin kungiyar har na tsawon shekaru tara da ƙarin albashi sama da shekaru 12.
Da yake zantawa da manema labarai jim kaɗan bayan taron gaggawa na majalisar da ta gudanar a Lafia babban birnin jihar, shugaban kungiyar a jihar, Dakta Peter Attah, ya bayyana cewa sun yanke shawarar dakatar da yajin aikin gargaɗi na kwanaki biyar domin rage wahalhalun da al’ummar jihar suka shiga.
Attah ya ce kungiyar ta umarci mambobinta da su koma bakin aiki cikin gaggawa domin ceton rayuka.
Idan za a iya tunawa, tun a ranar 13 ga watan Yunin 2023 ne kungiyar ta ba da wa’adin kwanaki 21 don biya mata bukata kafin ta shiga yajin aikin na gargaɗi.