fidelitybank

Likitoci ku yi ƙoƙarin janye yajin aiki – Gwamnati

Date:

Gwamnatin tarayya ta yi kira ga mambobin kungiyar likitoci ta kasa masu neman ƙwarewa NARD, da su janye yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai.

Karamin Ministan Lafiya Dr Tunji Alausa ne ya yi wannan kiran a ranar Alhamis a Kaduna yayin wata ziyara da ya kai cibiyar kula da ido ta kasa.

A cewar Alausa, ana ci gaba da tattaunawa don tabbatar da tsaron abokin aikinsu da aka sace, Dokta Ganiyat Popoola an sake ta.

“Muna kan maganar kuma mun tattauna da mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro Nuhu Ribadu game da lamarin.

“Na yi magana da kwamishinan ‘yan sanda kuma kowa yana aiki tukuru don ganin an sake ta,” in ji shi.

Ministan ya ce ya gudanar da taro a ranar Litinin da ta gabata da shugabannin NARD kan lamarin domin shawo kan su janye yajin aikin domin hakan zai kara dagula lamarin.

Alausa ya kara da cewa masu garkuwa da mutanen sun ci gaba da sauya bukatunsu a kowane lokaci amma jami’an tsaro suna bakin kokarinsu don ganin an ceto ta.

Idan dai za a iya tunawa ‘ya’yan kungiyar sun fara yajin aikin gargadi na kwanaki bakwai domin ganin an ceto wani likita mazaunin Kaduna, Dokta Ganiyat Popoola.

An yi garkuwa da Popoola, ma’aikaciyar cibiyar ne a watan Disamba, 2023 kuma yanzu ya shafe kusan watanni tara a gidan masu garkuwa da mutane.

A halin da ake ciki, shugaban kungiyar na cibiyar kula da ido ta kasa Dr Ibrahim Mohammed ya ce har yanzu yajin aikin na ci gaba da yaduwa.

Ya ce masu ba da shawara kan harkokin kiwon lafiya da na hakori ne suka shiga yajin aikin kuma umarni ne daga hukumar ta kasa.

news nigeria

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp