fidelitybank

Likitan da ya naushi mara lafiya yayin yi masa tiyata ya gamu da tutsu

Date:

Hukumomin China suna gudanar da bincike a wani asibiti inda aka samu wani likita da ake zargi da naushin mara lafiyar da yake tsaka da yi wa tiyata.

An ga lamarin ne cikin wani bidiyo da ya karaɗe shafukan sada zumunta a China, lamarin da ya fusata al’ummar ƙasar.

Asibitin na Aier China ya dakatar da likitan tare da korar shugaban asibitin da lamarin ya faru a 2019.

BBC ta tuntuɓi asibitin domin jin ta bakinsu.

Bidiyon ya nuna yadda likitan yake naushin mara lafiyar a ka sau uku yayin da yake tiyata a idonsa.

Aeir China da ke tafiyar da asibitocin ido da dama, ya ce lamarin ya faru ne lokacin wata tiyata a asibitinsa da ke Guigang a kudu maso yammacin China.

Mara lafiyar mace ce ƴar shekara 82 kuma yayin tiyatar saboda allurar kashe zafi da aka yi mata, ta sa a lokuta da dama ta yi ta motsa kanta da kuma ƙwayar idonta, kamar yadda wata sanarwa daga asibitin ta bayyana.

Hukumomi a yankin sun ce mara lafiyar ta ji rauni a goshinta. Kuma ba ta jin wani yaren sai na garinsu sannan ba ta gane gargaɗin da likitan yake mata ba a harshen Mandarin, lamarin da ya sa likitan ya yi yadda yake so da ita a lokacin gaggawa.

Bayan tiyatar, asibitin ya nemi afuwa tare da biyan yuan 500 – kwatankwacin dala 70 a matsayin diyya, a cewar ɗan matar wanda ya yi wa kafafen yaɗa labaran ƙasar bayani.

Ya kuma ce mahaifiyarsa a yanzu ba ta gani da idonta na hagu, sai dai babu tabbacin ko hakan ya faru ne saboda lamarin da ya faru.

A jiya Alhamis ne aka sanar da korar shugaban asibitin na Guiyang da kuma dakatar da likitan – wanda shi ma babban jami’i ne a asibitin saboda take ƙa’idojin aiki.

Duk da lamarin ya faru a Disambar 2019, batun ya fito fili ne a wannan makon bayan fitacciyar likita a China, Ai Fen ta wallafa bidiyon tiyatar da na’urar CCTV ta naɗa.

Dr Ai, wadda ke cikin tawagar likitocin da suka ankarar da jama’a kan ɓarkewar cutar korona a Wuhan, ta wallafa bidiyon a shafinta na Weibo inda mabiya sama da miliyan biyu suka kalla.

nigeria.news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp