Wata kotu a Libya ta ɗaure wasu mutane 37 da aka samu da laifin safarar mutane – bayan mutuwar bakin haure 11 da suka nutse a tekun Mediterrenean.
An yanke wa mambobin kungiyar biyar hukuncin ɗaurin rai-da-rai – wasu kuma ɗaurin shekara ɗaya zuwa 15.
Dukkansu suna da hannu wajen shirya wani rugujajjiyar jirgin ruwa da ya kamata ya kai baƙin hauren zuwa Italiya. In ji BBC.
Kungiyoyin kare hakkin bil adama sun ce da yawa daga cikin baƙin hauren suna fuskantar cin zarafi a hannun masu safarar mutane da kuma cikin cibiyoyin tsarewa na gwamnati.
Libya dai na fama da rikici da kum yamutsi tun bayan hamɓarar da gwamnatin Kanar Muammar Gaddafi a shekara ta 2011.