Tawagar kwallon kafa ta ƙasar Libya na ci gaba da atisayen buga wasa da Najeriya a wasan neman shiga gasar cin kofin Afirka ta 2025.
Tawagar ta gudanar da atisayen ne a yammacin ranar Litiin a filin wasa na Benina International Stadium.
Sai dai haka na zuwa ne a daidai lokacin da tawagar Super Eagles ta Najeriya ta yanke shawarar cewa ba za ta buga wasa da Libya ba bayan sun tsinci kansu cikin wani yanayi da suka shafe kusan awa 15 a filin jirgin sama na Abraq da ke Libya.
Tuni dai Super Eagles ta koma gida Najeriya yayin da ita kuma hukumar kwallon ƙafa ta Afrika CAF ta sanar da cewa ta fara bincike kan rikita-rikatar.