fidelitybank

Libya na buktara daukin gaggawa – MDD

Date:

Babban jami’in agajin gaggawa na Majalisar Ɗinkin Duniya, Martin Griffiths, ya ce matsalolin da ake fuskanta a Libya sanadin ambaliyar ruwa su ne: matsuguni da abinci da kuma buƙatun kula da lafiya.

Mista Griffiths ya ce ba a san girman bala’in da ya faru ba, saboda rarrabuwar kawuna tsakanin masu mulkin ƙasar, kuma a cewarsa ya zama wajibi a samu hadin kai tsakanin ɓangarorin biyu.

Da yake jawabi yayin wani taro a birnin Geneva, babban jami’in ya zayyano manyan ƙalubalan da ya ce hukumomin bayar da agaji na fuskanta a Libya.

Ya ce “Ina jin, matsalar da muke da ita a Libiya, ita ce samar da haɗin kai tsakanin gwamnatoci guda biyu a Libiya.

Na biyu shi ne tabbatar da gano haƙiƙanin tushen matsalar da ake ciki. A yanzu ba ma cikin Libiya, saboda haka ba za mu iya sanin girman matsalar ba, ambaliyar ruwan da asarar da aka tafka waɗanda suka shafi dukiya da gidajen jama’a da suka rushe.”

“Hakan ya sa hankali ya karkata ta yadda ba za a iya tantance ainihin bukatar da ake da ita da kuma gane adadin waɗanda suka mutu ba,” in ji shi.

“Ga kuma bukatar tabbatar da kayan agaji sun isa ga mabukata, kuma akan lokaci. Wannan ne ma ya sa haɗin kai ke da muhimmanci.”

“Babu wanda zai iya sanar da kai iya yawan ta’adin da iftila’in ya haifar saboda farraƙar da ake da ita a Libya.

Hamid Al-Mabrouk Abdel-Rahman, ƙwararren likitan masu fama da taɓin ƙwaƙwalwa ne, ya ce ayarin abokan aikinsa za su ziyarci biranen da ke kusa da gaɓar teku.

“Mun durfafi biranen Benghazi da Derna da kuma Al-Bayda, waɗanda lamarin ya shafa domin bayar da agaji ga mutanen da suka samu kansu a wannan bala’i.”

A cikin jami’an, akwai likitocin ƙashi da likitocin fiɗa da ma’aikatan jinya da ƙwararru a ɓangare tsafta, sun shirya domin yin aiki kafa-da-kafada

Ƙungiyar ba da agaji ta Red Crescent a Libya, ta ce bayan aukuwar ambaliyar ruwan, har yanzu ba a cire fatan samun ƙarin wasu da rai ba, duk da yake, tuni aka bayyana mutuwar akalla mutum 11,000, baya ga ɓatan ƙarin wasu dubban.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp