fidelitybank

Libya na azabtar da ‘yan Nijar 300 a gidan kurkuku – Alhaji Sani

Date:

‘Yan ƙasar Nijar, aƙalla 300 ne ake zargin hukumomin Libiya sun kama tare da tsare su a cikin wani mawuyacin hali na rashin kula tsawon wata da watanni.

A cikin wani bidiyo da ake ta yaɗawa ta shafukan sada zumunta an ga ɗaruruwan mutanen cunkushe a cikin wani ɗaki suna kira ga hukumomin ƙasar ta Nijar da su kai masu ɗauki.

Shugaban hukumar ƙoli ta ‘yan Nijar mazauna Libya, Alhaji Sani ya tabbatar da cewa bidiyon na gaskiya ne, mutanen an kama su ne wasu a wajen aikinsu wasu kuma sun shiga ƙasar a kan hanyarsu ta zuwa Sabha aka kama su.

Alhaji Sani wanda ya koka da halin da ‘yan Nijar ɗin ke ciki ya ƙara da cewa ba ma a nan kaɗai ake tsare da ‘yan Nijar ɗin a Libya ba akwai wasu ma a babban birnin ƙasar ta Libya, Tripoli waɗanda ya ce tun ma kafin azumi suke tsare.

Ya ce ba abin da ba su yi na ganin hukumomin Nijar sun kawo musu ɗauki sun shiga lamarin a sake su amma hukuma ba ta yi hakan ba.

Yanzu dai ƙungiyoyin fararen hula da na kare haƙƙin bil’Adama a Nijar ɗin sun shiga kira ga gwamnatin sojin Nijar da ta yi abin da ya dace a kan lamarin.

tribune newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp