Kwamishiniyar noma ta jihar Legas, Miss Ruth Abisoye Olusanya, ta shawarci masu ruwa da tsaki da su hada kai, don ganin rikicin kasar Ukraine bai kara ta’azzara matsalar karancin abinci a kasar ba.
Ruth ta yi gargadin cewa, nan ba da jimawa ba farashin Burodi zai kai ga hannun talaka.
Da ya ke jawabi a wani taron manema labarai na ranar dazuzzukan duniya a Legas, Olusanya ya sanar da cewa, tuni lamarin ya kara ta’azzara hauhawar farashin kayayyakin abinci da kuma kara tabarbarewar fatara.
Ba tare da daukar matakan da suka dace ba don magance wadata da arha na alkama, ta lura cewa, rikicin na iya yin illa ga yanayin Burodi.